Hausa: Unlocked Literal Bible - Hausa Print

Updated ? hours ago # views See on WACS
Littafin Amos
Littafin Amos
Sura 1

1 Waɗannan sune abubuwa game da Isra'ila wanda Amos, ɗaya daga cikin makiyaya a Tekowa ya karɓa a wahayi. Ya karɓa waɗannan abubuwa a kwanakin da Azariya ke mulkin Yahuda, da kuma kwanakin Yerobowam ɗan Yehowash ke sarautar Israila, shekaru biyu kafin girgizar ƙasa. 2 Ya ce, "Yahweh zai yi ruri daga Sihiyona; zai yi tsawa da murya mai ƙarfi daga Yerusalem. Wuraren kiwo na makiyayan za su bushe; ƙwanƙolin Karmel zai yi yaushi." 3 Wannan shi ne abin da Yahweh yace: "Domin zunubai uku na Damasku, har don huɗu ma, Ba zan janye hukuncin ba, domin sun zalunci mutanen Gileyad da maƙamai na ƙarfe. 4 Zan aika da wuta a kan gidan Hazael, kuma za ta cinye kagarar Ben-hadad. 5 Zan karya makaran kyamran Damasku zan kuma kau da mutumin da ke rayuwa a Kwarin Aben, da kuma mutumin da yake rike da sandar girma a Bet Iden. Mutanen Aram za su tafi bauta a Kir," inji Yahweh. 6 Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Gaza har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, domin su ne suka ɗauke kamammun mutane dukka, don su miƙa su ga mutanen Idom. 7 Zan aika da wuta akan garun Gaza, za ta kuma lakume kagarorinta. 8 Zan yanke mutumin da yake rayuwa a Ashdod da kuma mutumin da ya ke riƙe da sandar girma daga Ashkelon. Zan juya hannu na gãba da Ekron, kuma sauran Filistiyawa za su hallaka," inji Ubangiji Yahweh. 9 Wannan shi ne abin da Yahweh yace: "Domin zunubai uku na Taya, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don sun miƙa dukkan mutanen zuwa Idom, kuma sun karya yarjejeniyar yan'uwantakarsu. 10 Zan aika da wuta akan garun Taya, kuma za ta ƙone kagarorinta." 11 Wannan shi ne abin da Yahweh yace, Domin zunubai uku na Idom, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don ya farauci 'ɗan'uwansa da takobi ya kuma kawar da dukkan tausayi. Ya cigaba da fushi, fushinsa ya ɗore har abada. 12 Zan aika da wuta akan Teman, kuma za ta cinye fadodin Bozra." 13 Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na mutanen Ammon, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don sun farke mata masu ciki na Gileyad, saboda su ƙara faɗaɗa yankinsu. 14 Zan kunna wuta a garun Rabba, kuma za ta cinye fadodin, tare da ihu a ranar yaƙi, tare da rugugin hadari a ranar guguwar. 15 Sarkinsu zai tafi zuwa bauta, tare da sauran jami'ansa," inji Yahweh.

Sura 2

1 Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Mowab, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, don ya ƙone ƙasusuwan sarkin Idom zuwa toka. 2 Zan aika da wuta akan Mowab, kuma za ta cinye kagarorin Keriyot. Mowab zai mutu a hargitsi, tare da sowa da kuma busa ƙaho. 3 Zan lalata mai shari'a a cikinta, zan kuma kashe dukkan 'ya'yan sarki tare da shi," inji Yahweh. 4 Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Yahuda, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, domin sun ƙi dokar Yahweh kuma sun ƙi dokokinsa. Ƙarerayinsu sun jawo su yin tafiya ba dai dai ba, kamar yadda ubanninsu su ka yi tafiyar. 5 Zan aika da wuta akan Yahuda, kuma za ta cinye kagarorin Yerusalem." 6 Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Domin zunubai uku na Isra'ila, har ma don huɗu, ba zan janye hukuncin ba, domin sun sayar da salihai don azurfa da kuma masu bukata akan takalma. 7 Sun tattake kawunan talakawan kamar mutane na taka ƙura a ƙasa; suna ture matalauta a gefe. Mutum da ubansa su kwanta a wurin budurwa ɗaya kuma su na ɓata sunana mai tsarki. 8 Sun kwanta a gefen kowanne bagadi akan tufafin da aka bayar jingina don bashi, kuma a cikin gidajen Allahnsu sukan sha ruwan inabin waɗanda aka yi wa tãra. 9 Ga shi na hallakar da Ba'amore a gaban ku, dogaye masu tsawo kamar itatuwan sida; ya na da ƙarfin kamar rimaye. Ga shi na lalata 'ya'yan itatuwansa na sama da jijiyoyin ƙasa. 10 Kuma na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma bi da ku a cikin daji shekaru arba'in, na kuma ba ku ƙasar Amoriyawa. 11 Na ta da annabawa daga cikin 'ya'yanku, waɗansu kuma daga cikin samarin sun zama Naziriyawa. Ko ba haka ba ne, ya ku mutanen Israila? Yahweh ne ya faɗa 12 Amma kun sa Naziriyawa shan ruwan inabi kun kuma umarci annabawa da kada su yi anabci. 13 Duba, zan ragargaza ku kamar yadda amalanke cike da hatsi yake ragargaza mutum. 14 Ko wani mai gudu ma ba zai tsere ba, mai ƙarfi ba zai ƙara wa kansa ƙarfi ba; ko mai iko ya ceci kansa. 15 Mai baka ba zai iya tsayawa ba; mai saurin gudu ba zai tsira ba; mahayin doki ba zai ceci kansa ba. 16 Ko ma sojojin da suka fi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan - wannan furcin Yahweh ne.

Sura 3

1 Ku saurari maganar da Yahweh ƙe faɗa akan ku, ku mutanen Isra'ila, akan dukkan iyalinku, na fito da ku daga ƙasar Masar. Ku kaɗai na zaɓa daga kowanne iyalai a duniya. 2 "Saboda haka zan hukunta ku don zunubanku." 3 Zan yiwu mutanen biyu su yi tafiya tare, ba tare da yarda ba? 4 Zai yiwu zaki yayi ruri a daji ba tare da ya sami kome ba? Zai yiwu ƙaramin zaki yayi gurnani a kogonsa idan bai kama kome ba? 5 Zai yiwu tsuntsu ya faɗi akan ƙasa idan ba a kafa masa tarko ba? Zai yiwu tarko ya zargu daga ƙasa idan bai kama wani abu ba? 6 Zai yiwu mutane su rasa firgita idan suka ji ƙarar ƙaho a birni? Zai yiwu wata masifa ta auko wa birnin amma Yahweh bai aiko ta ba? 7 Hakika Ubangiji Yahweh ba zai aikata komai ba ba tare da ya baiyana wa bayinsa annabawa ba. 8 Zaki yayi ruri wane ne ba zai ji tsoro ba? Ubangiji Yahweh yayi magana; wane ne ba zai yi anabci ba? 9 A yi shelar wannan a kagarar Ashdod da kuma kagarar ƙasar Masar; a ce, "Ku tara kanku akan duwatsun Samariya ku ga babban shashanci a cikinta, da kuma irin danniyar da ke cikinta. 10 Domin ba su san abin da ya ke dai dai ba - wannan furcin Yahweh ne. Sun cika da tashin hankali da barnar kagarorinsu." 11 Saboda haka, wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh yace, "Abokin gãba zai kewaye ƙasar. Zai nuna ƙarfinsa ya rushe kagarorinka." 12 Wannan ne abin da Yahweh yace: "Kamar yadda makiyayi ya kan ceci ƙafafu biyu kadai na tunkiya daga bakin zaki, ko gutsarin kunne, hakanan kuma ke ma daga cikin mutanen Isra'ila wanda yake zama cikin Samariya, a gefen taragon jirgi kaɗai ko a gefen gado." 13 Ku ji ku kuma shaida game da gidan Yakubu - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne, Allah mai runduna, 14 "A ranar da zan hukunta Isra'ila saboda zunubai, zan kuma hukunta bagadodin Betel. ƙahonin bagadi za su kakkarye su kuma fadi a ƙasa. 15 Zan lalata gidan hunturu tare da na bazara. Gidajen da aka yi da hauren giwa zasu lalace, babban gidan shi ma zai lalace, - wannan furcin Yahweh ne.

Sura 4

1 Ku ji wannan maganar, ku shanun Bashan, ku na cikin dutsen Samariya, ku dake danne matalauta, ku dake hallaka mabukata, ku dake cewa da mazajenku, "Kawo mana abin sha." 2 Ubangiji Yahweh ya rantse da sunansa mai tsarki, "Ku duba, ranaku na zuwa akan ku da za a tafi da ku da ƙugiya, na ƙarshenku tare da fatsar kifi. 3 Za ku fita ta wurin da ya tsage a jikin garun birnin, kowannenku zai tafi ta cikin tsaguwar, za a jefar da ku waje wajen Harmon - wannan furcin Yahweh ne." 4 Ku tafi Betel ku yi zunubi, tafi Gilgal ku ƙara zunubi, ku kawo hadayarku kowacce safiya, zakkarku kowane kwanaki uku. 5 Ku mika gurasarku shaidar haɗayar godiya; ku yi shelar baikon yaddar rai, ku sanar da su, wannan dai dai ne, gare ku mutanen Isra'ila - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne. 6 Na ba ku tsabtatattun hakora a cikin dukkan biraninku da kuma ƙarancin gurasa a dukkan wurarenku. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba - wannan furcin Yahweh ne. 7 Na kuma hana ruwan sama daga gare ku a lokacin da akwai sauran watanni uku a yi girbi. Na sa a yi ruwa a birni daya, kuma na sa ka da a yi ruwa a wani birnin. Ɗaya daga cikin sashen ƙasar an yi ruwa amma ɗaya sashen ba a yi ruwa ba ya bushe. 8 Birane biyu ko uku suna ƙishi har ma sun tafi neman ruwa a birnin, amma ba su ƙoshi ba. Amma duk da haka ba ku komo wurina ba - wannan furcin Yahweh ne. 9 Na sa ma ku ƙunci tare da darɓa da raɓa. Yawan lambunanku da gonakin inabinku da itatuwan ɓaurenku da itatuwan zaitun ɗinku fari sun laƙume su dukka. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba - wannan furcin Yahweh ne. 10 Na aika ma ku da annoba irin wanda na aika wa Masar. Na kashe samarinku da takobi, an ɗauke dawakanku, an cika hancinku da ɗoyi. Amma duk da haka kun ki juyo wa gare ni - wannan furcin Yahweh ne. 11 Na hallakar da biraninku kamar yadda Allah ya hallakar da Saduma da Gwamrata. Kamar sandar da aka fizge daga wuta. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba - wannan furcin Yahweh ne. 12 Domin haka zan yi wani abu mummuna a kanki, ya Isra'ila; shirya don ki sadu da Allahnki, Isra'ila! 13 Ku duba, wanda ya yi duwatsu ya kuma halicci iska, ya baiyana tunaninsa ga mutum, ya maida safiya duhu, ya auna wurare na Duniya. Yahweh, Allah mai runduna, shi ne sunansa."

Sura 5

1 Ku ji wannan maganar dana ɗauke ta kamar ta makoki da zan yi a kanku, gidan Israi'la. 2 Budurwa Isra'ila kin faɗi, ba za ki ƙara tashi ba, an yasheta a ƙasarta; ba wanda zai ta da ita. 3 Wannan shi ne abin da Yahweh yace, "Birnin da ya fita tare da dubu zai dawo da ɗari kaɗai, kuma wanda ya tafi da ɗari amma goma kaɗai za su rage na gidan Isra'ila." 4 Wannan shi ne abin da Yahweh ya ce da gidan Isra'ila: "Ku neme ni ku kuma tsira! 5 Kada ku nemi Betel; ko ku shiga Gilgal; ka da ku tafi Biyasheba. Gama babu shakka ita ma za ta tafi bauta, kuma Biyasheba za ta zama wofi. 6 Ku nemi Yahweh ku rayu, ko ya taso ma gidan Yosef kamar wuta. Zai kuwa laƙume, ba kuma wanda zai kashe ta a Betel. 7 Mutanen nan na juya adalci zuwa abu mai ɗaci kuma suna jefar da ayyukan adalci a ƙasa!" 8 Allah ya yi manyan taurari tare da haskensu; ya maida duhu haske; ya maida rana dare shi ne kuma ya kira ruwan teku; ya ƙwararo shi a fuskar duniya. Sunansa Yahweh ne! 9 Ya kawo hallaka a kan ƙarfafa don lalacewar ta kai kan kagarori. 10 Ku na ƙin duk wanda ya ƙwabe ku a ƙofar birnin, kuma tare da duk wanda zai faɗi gaskiya. 11 Domin kun matsa wa talakawa kuna ƙwace alkama daga gare su - koda yake kun gina gidajenku da dutse, ba za ku zauna a cikinsu ba. Kuna sha'awar gonakin inabinsu, kuma ba za ku sha ruwan inabin ba. 12 Domin na san yawan laifofinku, kuma da girman zunubanku - kuna wulakanta masu kirki, ku na karɓar rashawa ku na hanawa talakawa adalci a wurin shari'a. 13 Saboda haka mai hikima shiru yake a waɗanan lokatai, don mugun lokaci ne. 14 Ku nemi yin nagarta ba mugunta ba, saboda ku rayu. Don Yahweh, Allah mai runduna, ya kasance tare da ku, kamar yadda ku ka ce ya ke. 15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta, ku yi adalci a cikin majalisa. Watakila Yahweh, Allah mai runduna, zai yi wa sauran da su ka ragu na Yosef alheri. 16 Saboda haka wannan shi ne abin da Yahweh yace, Allah mai runduna, Ubangiji, "Za a yi kuka da kururuwa a kowanne wurin taruwa za su kuma ce a dukkan tituna, 'Kaito! Kaito!' Za su kira manoma su yi makoki kuma masu makokin su yi kuka mai zafi. 17 A cikin dukkan gonakin inabinku za a yi kuka da kururuwa, don zan wuce a tsakiyar ku," inji Yahweh. 18 Kaito ga ku dake marmarin zuwan ranar Yahweh! Me ya sa ku ke jiran ranar Yahweh? 19 Za ta zama baƙa bakikirin kuma babu haske, kamar wanda ya gujewa zaki ya fada a bakin damisa, ko kuwa kamar wanda ya komo gida ya sa hannunsa a bango, maciji kuma ya sare shi. 20 Ko ranar Yahweh za ta zama haske ne ba duhu ba? Almuru ne ba haske ba? 21 Na ki bukukuwanku ba na murna da tarurukanku. 22 Ko da ya ke kun kawo mani baikon ƙonawa da baikonku na hatsi ba zan karɓe su ba, ba kuma zan dubi tarurukan baye-bayenku na manyan dabbobinku ba. 23 Ku kawar mani da hargowar waƙoƙinku; ba zan saurari kaɗe-kaɗenku da bushe-bushenku ba. 24 Maimakon haka ku sa adalci ya kwararo kamar ruwa, adalci kuma ya zama kamar kogin da ba ya ƙafewa. 25 Gidan Isra'ila ko kun kawo mani hadaya da baye-baye a cikin jeji har shekaru ariba'in? 26 Duk da haka ku ka ɗauki siffofin Sakkut sarkinsu da Kaiwan, allolinku na taurari- gumakan da kuka yi wa kanku. 27 Saboda haka zan sa ku yi ƙaura gaba da Damaskus," inji Yahweh, wanda sunansa Allah mai runduna ne.

Sura 6

1 Kaiton waɗanda ke zama sake a Sihiyona, da ke da kariya a tudun ƙasar Samariya, da ku da kuke sanannun mutane da suka fi na kowacce al'umma, ga waɗanda gidan Isra'ila ke zuwa don taimako! 2 Shugabaninku sun ce, "Mu je Kalne mu duba, daga wurin ku je Hamat, babban birnin, sa'an nan har zuwa Gat ta Filistiyawa. Sun fi mulkokinku biyu daraja ne? Ko kuwa, yankin ƙasarsu ya fi naku ne?" 3 Kaiton waɗanda suka kawar da ranar masifa suka kuma sa mulkin hargitsi ya zo kusa. 4 Suna kwance kan gadajen hauren giwa suna jin daɗin miƙe jiki a dogayen kujerunsu. Sun ci naman 'yan raguna daga garke da naman 'yan maruƙa daga turke. 5 Suna raira waƙokin wofi da giraya; kuna amfani da kayan aiki kamar Dauda. 6 Suna shan ruwan inabi daga manyan kwanoni sa'an nan su shafe jikinku da mai mafi kyau, amma ba su yin makoki saboda lalacewar Yosef. 7 To yanzu sune na fari da zasu tafi bauta, kuma bukukuwanku da shagulgulanku zasu wuce. 8 Ni, Ubangiji Yahweh na rantse da kai na - wannan furcin Ubangiji Yahweh, Allah mai runduna, na ƙi girman kan Yakubu; ba na son kagaransa. Saboda haka zan miƙa birnin da duk abin dake ciki. 9 Ko da zai zama mutane goma ne suka rage a gida ɗaya, zasu mutu dukka. 10 Sa'ad da dangin mamacin ya zo don ya ɗauki gawar mamatan -wanda zan ƙone su bayan ya fitar da gawarwaki daga gidan - sai yayi kira ga wanda ya ke a cikin gidan, ko akwai wani kuma a nan? Idan wannan mutum zai ce, "A'a." Sai ya ce, "Ka yi shuru, don ba za mu ambaci sunan Yahweh ba." 11 Duba, Yahweh zai ba da umarni, babban gida buge shi za a yi ya ragargaje, ƙaramin gida kuma ya rushe. 12 Dawakai sukan yi gudu a ƙonƙolin duwatsu? ko da wanda zai iya huɗa da shanu a can? Duk da haka ku ka mai da adalci dafi kuma ku ka mai da nagarta mugunta. 13 Ku da kuke murna akan Lo Dibar, wanda yace, "Ba mu ɗauke Karnaim ta wurin ƙarfinmu ba?" 14 Ku duba zan ta da wata al'umma ta yi gãba da ku, gidan Isra'ila -- wannan shi ne furcin Ubangiji Yahweh, Allah mai runduna. Zasu ƙuntata ma ku tun daga Lebo Hamat zuwa kwarin Araba."

Sura 7

1 Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya nu na mani. Duba, ya sa fari sun yi cincirindo lokacin da aka fara yankan hatsi, duba lokacin girbin baya ne bayan an cire na sarki. 2 Bayan sun gama cinyen kowanne ɗanyen ganye a ƙasar, sai na ce, "Ubangiji Yahweh, idan ka yarda ka yi gafara, yaya Yakubu zai tsira? Don shi ƙarami ne ainun." 3 Yahweh kuwa ya dakatar da nufinsa. Ya ce, "Ba zai faru ba." 4 Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya nuna mani: Duba, Ubangiji Yahweh ya yi kira akan wuta ta shari'a. An busar da fili mai yawan gaske, ruwa mai zurfi a ƙarƙashin duniya an kuma lalata ƙasa. 5 Amma na ce, "Ubangiji Yahweh, idan ka yarda ka tsaya; Yaya Yakubu zai tsira? Don shi ƙarami ne." 6 Yahweh kuwa ya dakatar da wannan. "Wannan ma ba zai faru ba," inji Ubangiji Yahweh. 7 Wannan shi ne abin da aka nuna mani: Duba, Ubangiji ya tsaya gefen bango, yana rike da magwaji a hannunsa. 8 Yahweh yace da ni, "Amos, me ka gani? Sai na ce, "Magwaji." Sai Ubangiji yace, "Duba, zan sa magwaji a wurin mutanena Isra'ila. Ba zan sake barin su ba. 9 Wurare masu bisa na Ishaku za a lalace, wuraren sujada na Israila za su zama kufai, kuma zan yi gãba da gidan Yerobowam da takobi." 10 Sai Amaziya, firist na Betel, ya aika da saƙo zuwa Yerobowam sarkin Isra'ila: "Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a cikin gidan Isra'ila. Ƙasa ba za ta iya ɗaukan dukkan maganganunsa ba. 11 Wannan shi ne abin da Amos yace, 'Yerobowam zai mutu ta takobi, kuma babu shakka Isra'ila zai tafi bauta daga ƙasarsa.'" 12 Amaziya yace da Amos, "Mai gani, tafi da gudu. koma ƙasar Yahuda, a can za ka nemi gurasa ka ci ka kuma yi annabci. 13 Amma kada ka ƙara yin annabci a nan Betel don nan wurin yin sujadar sarki ne kuma gidan sarauta ne." 14 Sai Amos yace wa Amaziya, "Ni ba annabi ba ne ko ɗan annabi. Ni makiyayi ne, kuma mai lura da itatuwan ɓaure. 15 Amma Yahweh ya ɗauke ni daga kiwo sai ya ce da ni, 'Tafi, yi annabci ga mutanena Isra'ila.' 16 Yanzu ji maganar Yahweh. Ka ce; "Ka da ka yi annabci gãba da Isra'ila, kuma kada ka yi magana gãba da gidan Ishaku.' 17 Saboda haka ga abin da Yahweh yace, 'Matarka za ta zama karuwa a birni, za a karkashe 'ya'yanka maza da mata da takobi; ƙasarka za a gwada ta a kuma rarraba; kai kanka za ka mutu a cikin ƙasa marar tsarki, kuma babu shakka Isra'ila zai tafi bauta daga ƙasarsa.'"

Sura 8

1 Wannan shi ne abin da Ubangiji Yahweh ya nuna mani. Duba, ga kwandon itacen ɓaure na kaka! 2 Ya ce, "Me ka gani, Amos?" Na ce "Kwandon itacen ɓaure na bazara." Sai Yahweh yace da ni, "ƙarshen mutanena Israila ya zo; Ba zan sake barin su ba. 3 Waƙoƙin haikali za su zama na makoki. A wannan rana -- wannan furcin Ubangiji Yahweh ne -- gawawwaki zasu yawaita, a ko'ina za a jefar dasu waje. Shuru!" 4 Ku saurari wannan, ku da ku ke tattake masu bukata ku na fitar da matalautan ƙasar. 5 Sun ce, yaushe ne sabon wata zai wuce, saboda ko ma sake sayar da amfanin? Yaushe ne Asabar za ta ƙare, ko ma sake sayar da alkama? Za mu rage girman ma'aunin mu kuma ƙara farashi, yayin da muke zalunci da ma'aunin ƙarya. 6 Wannan zai sa mu sayar da alkama mara kyau, mu saye talakawa da zinariya, kuma masu bukata da takalma." 7 Yahweh ya rigaya ya rantse ta wurin fahariyar Yakubu, "Babu shakka ba zan manta da kowanne aikinsu ba. 8 Shin ƙasar ba za ta girgiza a kan wannan ba, dukkan wanda ke cikinta zai yi baƙinciki? Dukkan ƙasar za ta hau ta sauka kamar Kogin Nilu, kuma za ta juya ta kuma sake dulmiyewa, kamar kogin Masar. 9 Za ya zama kuwa a wannan rana - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - zan mai da rana ta faɗi da tsakar rana, zan kuma sa duniya ta duhunta a rana kata. 10 Zan mai da bukukuwanku makoki kuma waƙoƙinku su zama makoki. Zan sa maku tufafin makoki, in kuma sa kowa ya aske kansa. Zan sa ku yi makoki kamar iyayen da suka rasa ɗan su tilo, kuma ranar mai daci ce har karshen ta. 11 Duba, ranaku na zuwa - wannan furcin Ubangiji Yahweh ne - da zan aiko da yunwa a ƙasar, ba yunwa don gurasa ba, ko kishin ruwa, amma domin rashin samun sakon magana daga wurin Yahweh. 12 Zasu yi ta tangaɗi daga teku zuwa teku; zasu yi gudu daga arewa zuwa gabas suna neman sakon maganar Yahweh, amma ba kuma zasu samu ba. 13 A wannan rana kyawawan 'yan'mata da samari zasu faɗi saboda ƙishi. 14 Waɗanda suka yi rantsuwa da zunubin Samariya suka kuma ce, 'Muddin allahnku na raye, Dan,' 'Muddin hanyar zuwa Biyasheba nanan' -- za su faɗi kuma ba zasu ƙara tashi ba."

Sura 9

1 Na ga Ubangiji tsaye wajen bagadi, sai yace, "Bugi saman ginshiƙan don harsasan dukka su girgiza. Farfasa su gunduwa-gunduwa akan kowannen su, ni kuma zan kashe su da takobi. Babu ɗaya daga cikinsu da zai tsere. 2 Ko da za su nutse cikin Lahira, can hannu na zai kamo su. Ko da sun hau sama, zan sauko da su. 3 Ko da sun ɓuya a bisa kololuwar Karmel, can ma zan neme su in cafko su. Ko da sun ɓoye daga ganina a karkashin teku, can ma zan bada umarni ga maciji, shi kuma zai sare su. 4 Ko da sun tafi bauta ta hannun abokan gãbarsu, can ma zan bada umarni ga takobi, takobi kuwa za ya kashe su. Zan sa idanuna a kansu don azaba ba nagarta ba." 5 Ubangiji Yahweh mai runduna ya taɓa ƙasa har ta narke, dukkan waɗanda suke cikinta suna baƙinciki; dukkan abin da ke cikinta zasu tashi kamar Kogi, za ta kuma nutse kamar kogin Masar. 6 Shi ne ya gina matakansa a sammai, ya kafa maɓoyarsa a bisa duniya. Ya kira ruwan teku ya ƙwararo a bisa fuskar duniya, sunansa Yahweh ne. 7 "Ku ba kamar mutanen Kush ba ne gare ni, mutanen Isra'ila? - wannan furcin Yahweh ne. Ba na fito da Isra'ila daga ƙasar Masar da Filistiyawa daga Krit da Aramiyawa kuma daga Kir ba? 8 Duba, idanuwan Ubangiji Yahweh suna kan mulkin nan mai zunubi, kuma zan lalata su daga fuskar duniya, sai dai ba zan hallaka gidan Yakubu kakaf ba -wannan furcin Yahweh ne. 9 Duba, zan ba da umarni, zan kuma rairayi gidan Isra'ila a cikin al'ummai, kamar wanda yake tankaɗan hatsi, don kada a rage ko ɗan ƙaramin dutse ya faɗi a ƙasa. 10 Dukkan masu zunubi daga cikin mutanena za su mutu ta wurin takobi, waɗansu za su ce, 'Masifa ba za ta auko mana ko ta kusan ce mu ba!' 11 A wannan rana zan ta da rumfar Dauda wanda ta faɗi, zan toshe kafafe. Zan ta da lalatattun wurarenta, in kuma sake gina ta kamar kwanakin dă. 12 Ta haka zasu ci nasara ga waɗanda su ka ragu a Idom, da kuma dukkan al'ummai da suke kira da sunana - wannan furcin Yahweh ne - shi ne ya yi wannan. 13 Duba, kwanaki na zuwa - wannan furcin Yahweh ne - sa'ad da mai huɗa zai riga mai girbi, mai matse ruwa inabi kuma zai riga mai shuka iri nan da nan. Duwatsu zasu zubo da ruwan inabi mai zaƙi, dukkan tuddai kuma su kwararo da shi. 14 Zan dawo da mutanena Isra'ila daga bauta. Za su giggina biranensu da su ka rurrushe su kuma zauna a ciki, zasu dasa gonakin inabi su kuwa sha ruwan inabinsu, za su yi lambuna su kuma ci amfanin 'ya'yansu. 15 Zan dasa su a ƙasarsu, ba kuwa za a ƙara tumbuke su daga ƙasar da na ba su ba," inji Yahweh Allahnku.