Hausa: Unlocked Literal Bible - Hausa Print

Updated ? hours ago # views See on WACS
Littafin Obadiya
Littafin Obadiya
Sura 1

1 Wahayin Obadiya. Ubangiji Yahweh ya faɗi haka a kan Idom: Mun ji bayani daga wurin Yahweh cewa an aika da jakada a cikin al'ummai, da cewa, "Tashi tsaye! Bari mu tashi mu kai mata hari!" 2 Ga shi zan mayar dake 'yar ƙarama a cikin al'ummai, za a rena ki ƙwarai. 3 Girman kai na zuciyarki ya ruɗe ki, ke da ki ke zaune a can cikin kogunan dutse, cikin ƙayataccen gidanki; a cikin zuciyarki, kin ce, "Wane ne zai saukar da ni can ƙasa?" 4 Ko da zaki tashi sama kamar gaggafa, ko da zaki kai sheƙarki cikin taurari, zan sauko dake ƙasa, inji Yahweh. 5 Idan ɓarayi suka zo wurinki, idan 'yan fashi suka zo wurinki da daddare - dubi yadda za a maishe ki kufai! - ba za su saci abin da suke buƙata ba ne kawai? Idan masu tattara inabi suka zo, ba zasu rage kala ba? 6 Yadda aka bincike Isuwa, harma da abin da ya ɓoye dukka an bincike! 7 Dukkan mazajen da suka ƙulla amana da ke zasu kore ki har kan iyaka, mazajen da suke zaune lafiya da ke sun ruɗe ki, sun ci nasara a kan ki. Waɗanda suka ci abincinki sun ɗana maki tarko. Babu fahimta a cikinsa. 8 Yahweh yace a waccan rana, "Ba zan ce a hallaka ma su hikima daga cikin Idom ba, da masu ganewa daga cikin dutsen Isuwa ba?" 9 Jarumawanki zasu karaya, Teman, domin a datse kowanne mutum daga dutsen Isuwa ta wurin yankawa. 10 Saboda ta'addancin da aka yi wa ɗan'uwanki Yakubu, kunya za ta rufe ki, za a datse ki har abada. 11 A ranar da ki ka tsaya a ware ke kaɗai, a ranar da bãƙi suka kwashe dukiyarsa, bãƙi suka shiga ƙofofinsa, suka jefa ƙuri'a a kan Yerusalem, kema ki na kamar su. 12 Amma kada ki yi murna a cikin ranar ɗan'uwanki, a ranar da ya yi asara, kuma kada ki yi farinciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu; kada ki yi fahariya a ranar baƙincikinsu. 13 Kada ki shiga ƙofar mutanena a ranar masifarsu; kada ki yi murna a cikin ƙuncinsu a ranar bala'insu; kada ki washe dukiyarsu a ranar rushewarsu. 14 Kada ki tsaya a mararrabar hanyoyi, domin ki datse masu neman tsira da miƙa kuɓutattun mutanensa a ranar ƙuncinsu. 15 Gama ranar Yahweh ta kusa a kan dukkan al'ummai. Kamar yadda ki ka yi, haka za a yi maki, abin da kika yi zai dawo kanki. 16 Kamar yadda kika sha a kan dutsena mai tsarki, haka dukkan al'ummai za suyi ta sha. Za su sha su haɗiye su zama kamar basu taɓa kasancewa ba. 17 Amma a Dutsen Sihiyona za a sami waɗanda suka tsira, kuma zai zama da tsarki; gidan Yakubu kuma zasu mallaki mallakarsu. 18 Gidan Yakubu zai zama wuta, gidan Yosef kuma zai zama harshen wuta mai ci, gidan Isuwa kuma zai zama tattaka, za a ƙone su a hallakar da su. Ba wanda zai tsira daga gidan Isuwa, gama Yahweh ya faɗi." 19 Waɗanda suke daga Negeb zasu mallaki dutsen Isuwa, na Sefilah kuma za su mallake ƙasar Filistiyawa. Za su mallaki ƙasar Ifraim da ƙasar Samariya; shi kuma Benyamin zai mallaki Giliyad. 20 Masu zaman bauta na mutanen Isra'ila masu yawa zasu mallaki ƙasar Kan'ana har zuwa Zerefat. Masu zaman bauta na Yerusalem, waɗanda ke Sefarad zasu mallaki biranen Negeb. 21 Masu kuɓutarwa za su hau zuwa Dutsen Sihiyona za su yi mulki a ƙasar kan tudu ta Isuwa, mulkin kuma zai zama na Yahweh.